Mustapha Imrana Abdullahi
BABBAR jam’iyyar adawa a tarayyar Nijeriya ta bayyana sanarwar nada Gwamnan jihar Sakkwato a matsayin shugaban kungiyar Gwamnonin jam’iyyar ta PDP
An dai bayyana hakan ne a wajen wani taron da suka gudanar.
Tuni dai ‘ya’yan jam’iyyar suke tururuwa domin taya shi murna da yi masa fatan alkairi.
Shugaban PDP na jihar Katsina Honarabul Yusuf Salisu Majigiri ya bayyana Gwamna Tambuwal da cewa Gwarzo ne da ya san makamar aiki kuma yana yin aiki tukuru dare da rana.